Friday, May 11, 2007

Sa-in-sa Tsakanin Google Inc. da Hukumar Kasar Thailand

Kamfanin Google Inc. mai gidan yanan sadarwan Google da Youtube, ta mayar da jawabi kan cajin da Hukumomi a kasar Thailand suke mata na rashin girmama sarkin kasar, sanadiyyar wasu bayanai na bidiyo da gidan yanan sadarwanta na Youtube) ya watsa masu nuna cin mutunci ga gwamnati da kuma sarkin kasar Thailand gaba daya. Wannan tasa kasar Thailand ta rufe wannan gidan yanan sadarwa, babu mai iya shiga daga kasar, sanadiyyar wannan abu da ta kira "cin mutumci da rashin lura da hakkin sarkinsu." A cikin jawabin da ta fitar wannan mako, kamfanin Google Inc. tace ai ba dukkan faya-fayan bidiyon da aka watsa bane suka keta hurumin mai martaba ba. Cikin goma sha biyu da aka watsa, hudu daga ciki ne, a cewar Google Inc. suka nuna cin mutunci ga sarki. Sauran na shagube ne ga gwamnati kan abinda ya shafi mu'amala da bakin wasu kasashe da ke zaune a kasar.

Kasar Thailand dai a halin yanzu ta rufe wannan gidan yanan sadarwa na Youtube, kuma ta bukaci da a sanar da ita wanda ya zuba wadannan faya-fayai a gidan yanan. Gwamnatin sojan kasar Thailand dai ta kwace karagan mulki ne daga tsohon shugaban kasan, wanda tayi ikirarin cewa ba ya girmama mai martaba sarki, a shekarar da ta gabata. Za a samu karin bayani a nan.

No comments:

Post a Comment