Saturday, December 4, 2010

TAKAITACCEN TARIHIN “BABAN SADIK”

Wasu cikin masu karatu sun bugo waya suna neman in rubuta takaitaccen tarihi na don su karanta. Na basu uzuri kan cewa babu wani abin ji a cikin tarihi na, amma sun dage sai sun ji. Don haka na dan tsakuro muku wani abu cikin tarihin rayuwata.

Suna na Abdullahi Salihu Abubakar, an kuma haife ni ne a Unguwar Hausawa ta Garki Village da ke Karamar Hukumar Municipal, a babban birnin tarayya ta Abuja, cikin shekarar 1976. Shekaru na 34 kenan. Mahaifi na shi ne Malam Abubakar Salihu, shi kuma Salihu kakana ne. Asalin kakanni na (da ma sauran mazauna Unguwar Hausawa a Garki Village) daga Kano suke. Zama ne ya kawo su wannan wuri, wacce a wancan lokaci ta zama kamar zango, kusan shekaru dari biyu da suka gabata. Kuma ma saboda tsawon zamani da halin zamantakewa, a halin yanzu duk mun rikide mun zama Hausawan Abuja. Na yi makarantar Firamare, da Sakandare da kuma Jami’a duk a Abuja. A halin yanzu ina da digiri kan fannin Tattalin Azkirin Kasa (Economics), wanda na samu daga Jami’ar Abuja. Ina kuma kan neman ilmin Kur’ani da sauran fannonin Ilmin musulunci har yanzu.

Ni mutum ne mai sha’awar rubuce-rubuce da karance-karance. Ina kuma son binciken ilmi kan fannonin ilmi irinsu Tattalin Arzikin Kasa (Economics), da Fasahar Sadarwar Zamani (Information Technology), da Fasahar Intanet, da Tsarin Harsuna (Linguistics), da Fassara (Translation), da Aikin Jarida (Journalism) da Kimiyya (Science) da dai sauran fannoni masu nasaba da wadannan. Allah Ya hore min juriyar karatu da rubutu iya gwargwado. A halin yanzu na rubuta littafi kan fasahar Intanet, mai suna “Fasahar Intanet a Sawwake”, wanda ake gab da bugawa. Akwai kuma wadanda nake kan rubutawa a halin yanzu, kamar “Tsarin Mu’amala da Fasahar Intanet”, da kuma “Wayar Salula da Tsarin Amfani da Ita”. Sai kuma kasidun da nake rubutawa a wannan shafi a duk mako.

A halin yanzu ina zaune ne a Sabon Garin Garki (watau New Garki Town) da ke nan Abuja. Ina da mata daya, da ‘ya’ya uku: Abubakar Sadiq, da Nabeelah, sai kanwarsu Hanan. Wannan shi ne dan abin da ya samu.

5 comments: