Monday, September 7, 2009

Wasikun Masu Karatu

Malam na ziyarci sabon shafin matambayi-ba-ya-bata na “Bing”, sai ya kasa bude min wani gidan yanar sadarwa, amma Google ya bude shi. To shin me ya ja haka ne? – Ahmad Muhammad Amoeva, Kano: 08066038946

Malam Ahmad ban fahimci tambayarka ba sosai. Ai gidajen yanar sadarwa na Matambayi-ba-ya-bata basu budo maka gidajen yanar sadarwa kai tsaye, sai dai su nemo maka abinda ka tambaye su, ta hanyar Kalmar da ka jefa musu. Idan kuwa suka aiko maka da jawabin tambayarka (Search Results), to ya rage wa kwamfutarka ta budo maka; ba hakkin gidan yanar da ya nemo maka rariyar da kake so bane. Ta yiwu a lokacin da ka tambaya, ko ka nemi shafin da aka nemo maka ya bude, siginar Intanet da ke tattare da kwamfutarka ta dauke, sai daga baya ta dawo. Allah sa na fahimce ka sosai.

Salam Baban Sadik, ya aiki don Allah ya ake saita Imel a waya, kuma idan Imel ya dade ba a yi amfani dashi ba yana lalacewa? - Bashir Ahmad, Kano: 08032493020

Malam Bashir barka da war haka, na kuma gode da sakonninka, ina samunsu sosai. Na kuma tabbata ka samu amsar wannan tambaya taka, wacce na aika nan take bayan ka aiko da wannan sako. A gaida su Umma da kowa da kowa. Na gode.

Assalaamu Alaikum, Abban Sadiq ya kokari? Allah yasa mu dace, amin. Malam ni dai har ya zuwa wannan lokaci shiru nake ji kan kumbon Nijeriya, wanda ya bace. Ina aka kwana ne a kan maganarsa, ko kuma ya bi shanun sarki shikenan? - Khaleel Nasir Kuriwa Kiru, Kano: 07069191677 (GZG274)

Malam Khaleel watakil ka mance. Ai a wannan shafin muka sanar da matsayin da gwamnatin tarayya ta dauka, cewa an daidaita da kamfanin da ya gina wancan kumbon da ya lalace (ba bacewa yayi ba), zasu sake gina wani a madadinsa, da ma wasu guda biyu da aka shirya dasu tun kafin nan. Wannan shine abinda hukuma ta sanar. Da fatar ka gamsu.

Baban Sadik, muna amfana da rubuce-rubucenka a wannan jarida ta AMINIYA mai albarka. Allah yayi sakayya. A ci gaba. - Abdullahi Aminu (Baban Auwal), Keffi, Nassarawa: 08035974923

Malam Abdullahi muna godiya da irin wannan karfafa gwiwa da ake mana. Tabbas babu wanda ya cancanci yabo da musamman irin Allah madaukakin sarki, wanda ke horewa da kuma sawwake lokaci da damar yin hakan. Muna kara godiya gareshi. Mun gode.

NEMAN AFUWA KAN ZIYARA

Na tabbata masu karatu basu mance ba da sanarwar da na bayar makonni uku da suka gabata, cewa zan kawo ziyara a Katsina da Zariya. Ina gab da yin hakan ne sai rikice-rikicen da suka faru a wasu jihohin Arewa suka bullo, don haka na dakata. A halin yanzu kuma aiyuka sun sake dabaibaye ni. In Allah ya yarda zan sake sanarwa idan na na tabbatar da tafiyar. Don haka a min hakuri, kuma ina godiya ga wadanda suka rubuto ko aiko sakonnin tes don min maraba. Allah Ya hada fuskokinmu da alheri, amin.

No comments:

Post a Comment