Tuesday, January 23, 2007

Sanarwa!

Majalisar Marubuta Littafan Hausa na Intanet (http://groups.yahoo.com/group/marubuta) ta fara shirye-shiryen bukin karrama marubuta littafan Hausa daga shekarar 1934 – 2006. A halin yanzu ana kan aiko da sunayen alkalan da zasu tantance gwarazan marubutan ne, wanda za a gudanar a majalisar a wani lokaci da za a ambata nan gaba. A kan gudanar da zaben net a hanyar Imel, da zaran an samu gwani kuma, sai a shirya gagarumin biki don mika kyaututtuka ga wadanda suka yi nasara. Don haka, duk mai sha’awar shiga wannan gasa/buki, yana iya shiga majalisar a adireshin da ke sama.

No comments:

Post a Comment