Wednesday, February 13, 2013

Rayuwar Matasanmu a Dandalin Facebook (1)



Wata Sabuwar Duniya

Idan masu karatu basu mance, a shekarar da ta gabata ne muka kawo kasida mai shafi goma, mai teken: Dandalin Facebook a Mahangar Binciken Ilmi. A ciki mun yi bayani filla-filla kan asali da samuwar wannan dandali, da yadda ake rajista, da yadda ake mu'amala da shafin, da kuma wasu daga cikin matsalolin da ke tattare da dandali a mahanga mai fadi.  A yau ga shi mun dawo ne don kara bayani kan abin da ya shafi matasanmu, da irin rayuwar da suke yi a dandalin, wanda hakan zai fahimtar da mu wasu abubuwa masu muhimmanci, musamman kan mummunar tasirin wannan dandali kan tunani da fahimtar matasanmu.  Kafin mu yi nisa, ina son masu karatu su fahimci cewa wannan kasida ta fadakarwa ce kawai, ba tonon asiri tazo yi ba.  Ba zan ambaci sunan kowa ba.

A bayyane yake cewa akwai matasanmu da yawa a dandalin Facebook.  Ba za ka san hakan ba sai ka shiga.  Za ka ga mutane, tsakanin 'yan mata da samari da tsofaffi da zawarawa da gagware wa tuzurai, duk sun yi rajista kuma suna sada abin da suke kira "zumunci."  Babban abin da ya sawwake yaduwarsu a wannan dandali kuwa dalilai ne guda biyu.  Abu na farko shi ne samuwar wayar salula a hannun jama'a, wanda ya game gari da duniya baki daya.  A Najeriya akwai layukan wayar salula sama da miliyan 90 a kididdigar shekarar da ta gabata.  A arewacin kasar akafi samun jama'a masu dauke da wayar salula.  Galibin wayoyin salular wannan zamani kuwa duk karancin kudi da araharsu, za ka samu suna dauke ne da hanyar sadarwa ta Intanet.  Wannan ya sa duk wanda ke da wayar salula a hannunsa, to kamar yana da shafin Facebook ne, domin yin rajista babu wahala.  Karin a kan haka, sai kamfanin Etisalat ya gina wata manhaja ta musamman na shafin Facebook, muddin ka shiga shafin, nan take za ka iya saukar da wannan manhaja, ka yi rajistar shafinka na facebook ba tare da wata matsala ba.  Sannan, ko babu ko sisi a wayarka kana iya shiga, in dai layin Etisalat kake amfani da shi.  Abu na biyu shi ne saukin mu'amala.  Shafin facebook yana da saukin mu'amala.  Wannan yasa duk wanda ya shiga sau daya sau biyu, ba ya bukatar wani darasi kuma. 

Manufofi

Wadannan dalilai biyu suka taimaka wajen yaduwar matasanmu a dandalin facebook.  Kowa na son ya shigo don ya nemi abokai ko 'yan mata, ko samari da dai sauransu.  A kasidar baya mun nuna cewa daga cikin amfanin dandalin facebook akwai sadarwa, da yin abota, da samar da sanayya mai amfani da amfanarwa, da fahimtar rayuwa ta hanyar kallon yadda wasu ke tafiyar da rayuwarsu a duniyar da suke.  Har a yanzu akwai wadannan amfanoni basu gushe ba a dandalin facebook.  Akwai majalisu da matasanmu suka kafa, masu amfani sosai.  Akwai zaurukan tattaunawa na musamman masu amfani su ma.  Sannan kuma wasunsu sun samu hanya mafi sauki wajen yada addini da shari'ar musulunci.  Wasu sun yi abota ta Allah da Annabi. Wasu sun yi kawance ta Allah da Annabi.  Amma galibin mu'amalarmu, ina nufin mu matasan kasar Hausa, akwai alamar tambaya kanta.

Dandalin Abota, ko Dandalin Badakala?

Babban abin da yafi ban cikin al'amuran matasanmu a dandalin facebook shi ne, rashin manufa takamaime a yayin da suke shawagi da shantakewa a dandalin.  Abu na farko da aka sansu da shi shi ne yawan ruduwa da 'yan mata.  Duk wacce ka shiga shafinta a dandalin facebook in dai budurwa ce, za ka ga kashi 90 cikin abokananta maza ne.  Da zarar ta yi tari, ko "mhmm" ta rubuta a shafinta, nan take za ka ga ta'aliki (comments) daga maza sama da hamsin kafin sa'a guda.  Duk abin da tace sai an ce wani abu a kai.  balle ta loda hoto a shafin.  Ba sai na gaya muku abin da zai faru ba.  Su kansu 'yan matan haka suka fi so.  Musamman wasu ke daukan hotuna su loda a shafinsu, don su ji me samari za su ce.  Idan kana karanta sakonnin da matasa ke rubutawa dangane da wadannan hotuna sai ranka ya baci.  Wai duk nan yabonta ake.  Abu na biyu shi ne yaudara.  Su kansu wasu daga cikin 'yan matan karya suke yi, hotunan wasu suke lodawa suce nasu ne.  Su ma samarin suna haka. Don haka galibin samarinmu, ba duka ba, idan ka shiga shafukansu ba abin da za ka gani sai surutai kan 'yan mata, da wasannin kwallon kafa da hotunansu, da abubuwa marasa kima.  Wanda hakan ke nuna cewa mai wannan shafin ya shigo ne kawai don yayi ta walagigi mara ma'ana.

Abu na gaba shi ne cin mutuncin abokin magana.  Da yawa daga cikin matasa a dandalin  facebook ba su da da'a, musamman dai a majalisun da ake tattaunawa kan abubuwan da suka shafi al'umma. A daya daga cikin manyan majalisun da ke shafin facebook na matasanmu, na sha karanta zage-zage, da surutan cin mutuncin abokin zance; ba kunya ba tsoro.  A wasu lokuta sai na sa baki al'amuran ke sassautawa.  Wannan bai dace ba.  Sai kuma batun batsa da ashararanci.  Wannan kuma ya kasu kashi biyu.  Akwai zantuka da wasu matasanmu ke yi kan hotunan 'yan mata da niyyar yabo, ko kokarin gamsar da 'yan matan cewa suna da kyau.  Idan ka karanta ire-iren wadannan zantuka sai ranka ya baci. Sai kuma yaudara, wanda wannan ruwan dare ne a dandalin facebook. Da yawa cikin mutane kan rubuta abin da ba shi bane hakikanin rayuwarsu.  Wannan tasa idan kana karanta bayaninsu a "Profile" sai ka ga akwai tufka da warwara. Misali, yarinya ko matashi zai ce musulmi ne shi, mai son Manzon Allah, mai kishin musulunci, littafinsa shi ne Kur'ani da Hadisi, amma idan aka zo wajen "Hobbies" ko "Interests", watau abin da yake sha'awa a rayuwarsa ko rayuwarta, sai ka ga ya zayyana sunayen manyan makiyan Allah daga cikin mawakan turai, da miyagun fina-finan da a zahiri suna cin mutuncin addini ne, ko ma wasunsu duka cike suke da batsa da rashin tarbiyya.  Wannan tufka da warwara ne ko shakka babu.  Galibin matasa idan ka shiga "Profile" dinsu za ka ta cin karo irin wannan.

Abu na gaba shi ne yawan kankamba da fadi-ba a tambayeka ba.  Akwai majalisa ta musamman da ake amsa tambayoyi kan al'amuran addini, ma'ana majalisa ce ta fatawa dai a takaice.  Akwai wadanda aka killace musamman don amsa tambayoyi, wanda hakan ya kamata daman.  Tun da shari'ar musulunci na gudanuwa ne cikin tsari, sannan ba kowa bane ke da kudurar amsa fatawa, domin amana ce.  Amma abin mamaki da zarar wani ya aiko tambaya, kafin wadanda aka killace su bayar da amsa, nan take za ka mutum yayi caraf ya fara magana, a ciki yana cewa: "…a gani na abu kaza hukuncinsa kaza ne." Ko "…a fahimta ina ganin kaza zai zama kaza." Sai kace an nemi shawararsa.  Ya mance cewa ilmi amana ce, kuma ba a gudanar al'amuran addini da jahilci.  A wannan majalisar har wa yau, da zarar mace ta aiko tambaya, kafin a bayar da amsa nan take samari sama da goma sun fara tofa albarkacin bakinsu, duk dai don neman samun shiga.  Mun dauki addini abin wasa.

Abu na gaba shi ne rashin sirri.  Da yawa daga cikin matasa har yanzu sun kasa fahimtar mummunar hadarin da ke tattare da rashin sirri.  Idan kana son fahimtar hakan kuwa sai ka shigo dandanlin facebook.  Da wanda ke kwance a kan gado yana hutawa, da wanda ke cin tuwo miyar kuka, da wanda ke zance budurwarsa, da wanda ke shan shayi, da wanda ke kan hanyar tafiya zuwa wani garin, da wanda zai shiga wanka, da wanda ke sanya tufafi, duk za ka gani a facebook, matasanmu sun shigar.  Ba ruwansu da mai zai je ya dawo.  A sauran kasashen da suka ci gaba a fannin sadarwa, zantuka irin wadannan sun yi sanadiyyar mutuwar wasu, da hasaran rayuka, da ta'addanci, da rasa matsayin siyasa da shugabanci, da karyewar arziki, da mutuwar auratayya da dai sauransu.  To amma matasanmu ko a jikinsu, wai an tsikari kakkausa.  Kari a kan haka har da hotuna marasa kan gado. Wasu hotunan ma basu kamata a ce an nuna su ga duniya ba, amma a shafin facebook duk za ka gansu.

Abu na gaba shi ne kankamba wajen latse-latse da matse-matse.  A ka'idar yadda shafin facebook ke gudanuwa, duk halin da abokanka ke ciki ana sanar da kai ne.  Idan abokananka suka kalli wani hoto ko bidiyo da Intanet ta hanyar manhajar facebook, za a sanar da kai.  Matsalar ita ce, da zarar an sanar da kai, sai kaji kaima kana son ka kalla, da zarar ka matsa shikenan, hoton ko bidiyon ba zai bude ba, sai an kaika asalin shafin.  Ba wannan bane matsalar, galibin ire-iren wadannan hotuna da bidiyo na batsa ne, amma kai ba za gani  a fili, da zarar ka matsa, nan take za a kai wa abokanka sanarwa cewa ka kalli hoto ko bidiyo kaza, mai dauke da batsar, amma kai ba za ka gani ba.  Ka ga a nan kai baka ga wannan hoto ba, amma an kai wa abokanka sanarwa cewa ka gani.  Idan mai mutunci ne kai, kimarka ta zube kenan a idonsu.  Matasanmu duk basu lura da wannan.  Duk abin da muka ga ana yi sai kawai mu ma muyi, ko bamu san amfaninsa ba.  Wadannan kadan ne cikin badakalar da ke faruwa a 
dandalin facebook kan abin da ya danganci matasanmu.

Kammalawa

Kafin mu karkare, biyu daga cikin manyan dalilan da ke haddasa wadannan abubuwa kuwa su ne: samun sakakkiyar 'yanci, da kuma rashin tarbiyya.  Galibinmu idan muna dauke da wayar salula a cikin dakunanmu sai mu ga komai ma muna iya yi.  Sannan idan hakan ya hadu da rashin tarbiyya sai lamari ya lalace. Rashin tarbiyya ya kunshi tsarin tsara lokaci kan duk abin da muke yi.  Galibi muna shiga facebook ne kawai mu yi shashanci ba wai mu karu da wani sabon ilmi kan abin da bamu mallaka ba.  Wannan shirme ne.  abu na biyu shi ne rashin manufa.  Ba mu da manufa ta gari.  Abin da muka ga ana yi sai kawai mu buge da yi.  Meye amfaninsa?  Oho!  Wannan ya fi yawa a bangaren matasanmu maza.  Wajibi ne mu rika lura da manufarmu kan abin da muke yi a Intanet.  Duk abin da ba zai samar maka da wani alfanu ba, kayi hakuri dashi shi yafi alheri.  Allah sa mu dace.  

No comments:

Post a Comment