Wednesday, February 13, 2013

Wasu Daga Cikin Sakonninku



Assalaamu alaikum Baban Sadik, da fatan kana lafiya, Allah kara maka basira da hikima. Shin, me yasa idan aka boye lamba daga wayar salula, kuma aka turo sakon tes da ita, sai lambar ta bayyana a sakon?  -  Prince Sadiq Babanni, Yola.

Wa alaikumus salam, Malam Sadik barka da warhaka. A ka'idar aiwatar da kira da wayar salula, idan ka kira wani, za a nuna wa wanda ka kira lambarka a wayarsa, yana gani.  Amma idan kaje sashen Tsare-tsaren wayarka, watau "Settings", ka canza wannan tsari cewa kada ta rika nuna wa wanda ka kira lambarka, to za ta boye lambar.  Wannan a kira ne kadai ya tsaya.  Amma idan ka aika sakon tes dole za ta nuna.  Domin babu wani tsari na boye lambar wanda ya aiko tes a wayar salula.  Dole za ta nuna.  Da fatan ka gamsu.

Assalaamu Alaikum, barka da warhaka.  Yanzu don Allah kai Abdullahi Salihu Abubakar kace yin azumi a watan Rajab ba daidai bane?  A matsayinka na Musulmi? -  08031323908

Wa alaikumus salaam, na san kana ishara ne zuwa ga bayanin da nayi a cikin kasida ta mai taken: "Bunkasar Fasahar Sadarwar Zamani a Najeriya – Kalubale da Hanyoyin Ci Gaba," inda nake bayani cewa jama'a su yi hankali da sakonnin da ake turo musu ta tes musamman lokacin azumi kan falalar ayyuka, da cewa akwai hadisan karya da ake aikowa.  Idan ka fahimce ni, ban ce yin azumi a watan Rajab ba, nace kan "…falalar yin azumin Rajab."  Akwai bambanci tsakanin "yin azumi a watan Rajab, da falalar azumin Rajab."  Akwai hadisan karya sama da talatin da aka kaga aka ce Manzon Allah ne ya fada, masu nuna falalar watan Rajab.  A wasu kasashe bayan azumi, ana yanka dabba da ake kira "Ateerah", ana kwana sallah a tsakiyar watan, watau "Salaatur Ragaa'ib," ana rarraba gurasa da masa bayan an karanta musu Suratul Mulk, duk wannan bai inganta ba daga Manzon Allah.  Mu a nan abin da muka fi yi shi ne azumi, wanda muke kira azumin tsofaffi, da kuma sallar tsakiyar wata.  Amma yin azumin nafila cikin Rajab, kamar yadda aka saba yi a sauran watanni, ya halatta kuma ma abin so ne. musamman azumin litinin da alhamis, da yin azumi uku cikin kowane wata, duk sun inganta daga Manzon Allah. Amma idan da wancan manufa ce, cewa watan Rajab na da wata falala ta musamman, ba abin da ya inganta.  Don karin bayani ka duba littafin "Al-Fawaa'idul Majmoo'ah fil Ahaadeesil Mawdoo'ah" wanda Shawkaani ya rubuta, lambar hadisi na 287, da 288, da 289, da 290 da kuma 291.  Da fatan ka gamsu.

No comments:

Post a Comment